Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta tura korafe-korafen da aka gabatar kan Malam Lawan Triumph ga majalisar Shura

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta aika da korafe-korafen da aka gabatar mata kan kalaman Malam Lawan Triumph zuwa ga majalisar Shura ta jiha domin ta yi nazari a kansu.

 

Wannan na cikin sanarwar da mai magana da yawun Sakataren Gwamnati Musa Tanko, ya fitar, inda ya bayyana cewa kungiyoyin addini daban-daban suka shigar da korafe-korafen, ciki har da Safiyatul Islam, Tijjaniya Youth Enlightenment Forum, da kuma wasu kungiyoyin Ahlul Sunnah da Qadiriyya.

 

Sanarwar ta rawaito cewa sakataren gwamnati Alhaji Umar Farouk Ibrahim, ya ce, gwamnatin jihar ta kuduri aniyar tabbatar da zaman lafiya da mutunta juna tsakanin mabiya addinai. Ya kuma roki jama’ar Kano da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum cikin bin doka da oda.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!