Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta umarci sabbin jami’anta su gaggauta bayyana kadarorinsu ga CCB

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta umarci sabbin jami’an da aka naɗa a muƙamai su gaggauta bayyana kadarorinsu ga hukumar ɗa’ar ma’aikata ta Najeriya Code of Conduct Bureau CCB.

 

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim, ne ya bayyana haka a Kaduna yayin taron horas da manyan jami’an gwamnati  a ranar Asabar.

 

Ya ce wannan mataki na daga cikin manufofin tabbatar da gaskiya da adalci a harkokin gwamnati, tare da kare jama’a daga rikice-rikicen da suka shafi kudi da kuma tabbatar da gudanar da mulki na amana.

 

Ya ƙara da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf na ƙoƙarin tabbatar da cewa duk jami’an gwamnati suna aiki da tsoron Allah da riƙon gaskiya, inda ya bukaci sabbin jami’an su nuna kishin ƙasa ta hanyar bin wannan doka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!