Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano za ta haɗa gwiwa da Ghana don farfaɗo da ilimi

Published

on

Gwamnatin jihar Kano, ta ce, za ta yi haɗin gwiwa da ƙasar Ghana domin farfaɗo da harkokin ilimi.

Gwamnan Kano jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi baƙuncin ƙaramin ministan lafiya na ƙasar ta Ghana Alhaji Mahama Ase Asesini, wanda ya kai ziyara gidan gwamnatin Kano.

Abba Kabir Yusuf wanda ya kuma bayyana tsohuwar dangantakar da ke tsakanin alumar jihar Kano da kasar Ghana, yace gwamnatin kano zata farfado da dangantakar ne domin amfanar da alumar kasashen biyu.

Gwamnan, ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta gyara tare da samar da isassun kayan aiki a dukkan manyan asibitocin da ke ƙananan hukumomin Kano 44.

Da ya ke jawabi tun da farko, ƙaramin Ministan lafiyan na Ghana Alhaji Mahama Ase Asesini, ya ce, ya kai ziyarar ne domin farfaɗo da dangantar da ke tsakanin Kanawa da mutanen Ghana ta furskar al’adu da zamantakewa.

Rahoton: Umar Abdullahi Sheka

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!