Labarai
Gwamnatin kano zata tallafawa Almajirai da sanaoin dogaro da kai
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/05/Jigawa-Almajirai.jpg)
Gwamnatin jihar Kano ta ce ta yi hadin gwiwa da babban bankin kasa CBN domin samun rancen kuɗin da za ta sayi na’urar cirar kuɗi ta P.O.S a fadin jihar.
Tsohon sakataren gwamnatin Kano Alhaji Rabi’u Sulaiman Bichi, wanda kuma ya wakilci gwamnatin Kano a wajen taron wayar da kan malaman tsangaya.
Ya ce, za a ranci kuɗin ne wajen tallafawa dukkanin makarantu na tsangaya a jihar Kano, ta hanyar samarwa da ɗaliban sana’o’in dogaro da kai.
A cewar sa, gwamnatin ta kirkiro da tsarin ne domin a rage yawaitar barace barace a kan tituna.
Alhaji Sulaiman ya kuma ce, gwamnatin ta hada kai da babban bankin ƙasa domin a bude wuraren cire kudi ta cikin sauki ba sai mutun yaje banki ba.
You must be logged in to post a comment Login