Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ɓatan kuɗaɗen marayu: An dakatar da manyan jami’an kotunan Shari’ar Muslunci na Kano

Published

on

Hukumar ɗauka da ladabtar da ma’aikatan shari’a ta Kano ta dakatar da Akanta da Daraktan Kuɗi na kotunan Shari’ar Muslunci na jihar.

Hukumar ƙarƙashin Babban Jojin jiha Mai Shari’a Nura Sagir Umar ta sanar da dakatarwar ne a yau Litinin.

An dakatar da manyan ma’aikatan biyu ne sakamakon zargin badaƙalar ɓatan kuɗaɗen marayu har miliyan 345 daga asusun kotunan Muslunci.

Mai magana da yawun kotunan Kano Baba Jibo Ibrahim ya shaida wa Freedom Radio cewa, an dakatar da ma’aikatan har zuwa kammala bincike.

Idan zaku iya tunawa a ranar 13 ga watan Satumban da muke ciki ne, Freedom Radio ta bankaɗo badaƙalar ɓatan kuɗaɗen.

Ita ma hukumar yaƙi da rashawa ta Kano PCACC ta ce, tana bincike a kan ɓatan kuɗaɗen.

Ga cikakken labarin a nan

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!