Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Najeriya ta kare matakin da ta dauka na nada Ahmed Rufa’i Abubakar shugabancin hukumar leken asiri NIA

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta kare matakin da ta dauka na nada Ahmed Rufa’I Abubakar a matsayin sabon shugaban hukumar leken asiri ta kasa NIA.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan kafofin yada labarai Malam Garba Shehu ne ya bayyana haka ga manema labarai Asabar din da ta gabata a birnin tarayya Abuja.

Ya ce abin takaici ne matuka yadda wasu kafafen yada labaran Najeriya su ka bari ‘yan siyasa suna amfani da su domin biyan bukatun kansu.

Malam Garba Shehu ya kara da cewa babu wani jami’I da ya da ce da wannan mukafi da ya kai Ahmed Rufa’I Abubakar domin kuwa ya rike mukamai manya-manya a hukumar kafin ya bar aikin a kashin kansa bayan da ya samu mukamin darakta a majalisar dinkin duniya.

Babban mai baiwa shugaban kasar shawara ya kuma musanta cewa sabon shugaban hukumar ta NIA ya bar aikin ne sakamakon gaza cin jarabawa da ya yi har sau biyu, yana mai cewar idan mai magana wawa ne majiyin ta ba wawa bane.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!