Labarai
Gwamnatin Sojin Burkina Faso ta rushe jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyi

Gwamnatin sojin Burkina Faso ta rushe jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyi a ƙasar biyo bayan dakatar da su a shekarar 2022, sannan kuma za a miƙa duka ƙadarorinsu zuwa ga gwamnatin ƙasar, kamar yadda kafar gwamnatin ƙasar RTB TV ta ruwaito.
Rahotonni sun bayyana cewa, gwamnatin ta amince da dokar rushe jam’iyyun ne a zaman majalisar zartarwar ƙasar, wanda shugaban sojin mulkin soji Ibrahim Traore ya jagoranta.
Mai magana da yawun gwamnatin ƙasar, Pingdwende Gilbert Ouedraogo ya ce an ɗauki matakin ne bayan nazarin da aka yi kan rahoton binciken da aka gudanar domin inganta harkokin gwamnatin ƙasar, kamar yadda kafar Lefaso.net mai zaman kanta ta ruwaito.
Kafin juyin mulkin watan Satumban 2022 a ƙasar, akwai jam’iyyun siyasa kusan 100, inda guda 15 a ciki suke da wakilai a majalisar.
You must be logged in to post a comment Login