Connect with us

Labarai

Gwamnatin Sokoto ta yi taruka jin ra’ayin jama’a kan kasafin kuɗi

Published

on

Gwamnatin Jihar Sokoto, ta ƙaddamar da tarukan jin ra’ayoyin jama’a a mazabu uku na jihar domin shirin kasafin kuɗin baɗi.

 

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, taron da aka gudanar a Tambuwal da Tangaza da Gwadabawa, ya haɗa Sarakunan gargajiya da ‘yan majalisu da kungiyoyin matasa da na mata da kuma na masu bukata ta musamman domin tantance bukatun kowa.

 

Kwamishinan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Dakta Abubakar Zayyana, ya ce shirin na daga cikin manufar gwamnan jihar, Ahmad Aliyu na tafiyar da mulki a buɗe tare da tafiya da jama’a, wanda zai mayar da hankali kan bangarorin ilimi da kiwon lafiya da na samar da ababen more rayuwa da rage talauci a jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!