Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya na shirin ayyana dokar ta-baci a fannin lafiya

Published

on

Shugaba Tinubu

Gwamnatin tarayya ta ce za ta ayyana dokar ta-baci a ɓangaren lafiya a faɗin Najeriya sakamakon ƙalubalen da iskar Gas da dangogin sa ke haifarwa na dumamar yanayi.

Ministan muhalli Balarabe Lawal, ne ya bayyana hakan a birnin tarayya Abuja , a wani taron masu Ruwa da tsaki da Majalisar masana muhalli da kiwon lafiya ta kasa EHCON ta shirya kan kalubalen rashin lafiya da ake samu dalilin gurbata muhalli.

Da ya ke jawabi a yayin taron , Ministan wanda babban sakatare a ma’aikatar Mahmud Kambari, ya wakilta a taron ya ce matsalar ta wuce duk yadda ake tunani don haka gwamnatin tarayya ta ga dacewar ayyana daukar matakin gaggawa don magance matsalar.

Haka kuma, gwamnatin ta ce, za ta hada kai, da dukkanin masu ruwa da tsaki, musamman ma masana’antu da kamfanoni na zirga -zirga don ganin an samar da matakan da suka dace wajen amfani da Gas.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!