Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya na shirin tattaunawa don dakile yunkurin yajin aikin ASUU

Published

on

Gwamnatin Tarayya za ta kira taron tattaunawa na musamman domin dakile yiwuwar tsunduma yajin aikin kungiyar malaman jami’o’i ASUU.

Ana sa ran shugabannin kungiyar za su kira taron majalisar koli NEC, wanda zai yanke hukuncin ko ASUU za ta tsunduma yajin aikin ko a’a, bisa sakamakon tattaunawar da gwamnati za ta yi.

Wani babban mamba a majalisar kolin ta NEC a kungiyar ASUU, wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya zargi gwamnati da yin jinkiri da gangan domin hana kungiyar ɗaukar mataki.

Ya ce bayan ganawar gwamnati, ASUU za ta gudanar da nata taron NEC domin yanke mataki na gaba. 

Idan ba a manta ba dai, wa’adin da ASUU ta bai wa gwamnati ya kare a ranar Asabar din da ta gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!