Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yajin aikin : ASUU zata karbi Naira biliyan 30 daga gwamnati

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta amince ta biya kungiyar malaman jami’o’in kasar ASUU naira biliyan 30 a matsayin kudaden alawus.

Sai dai, Za’a soma biyan su kudaden ne daga watan mayun badi zuwa fabarairun shekarar 2022.

Zalika gwamnatin kasar za ta kashe naira biliyan 20 wajen farfado da bangaren ilimi a wani mataki na kawo karshen yajin aikin da kungiyar ta kwashe watannin 6 tana yi yanzu haka.

Wadannan dai na daga cikin yarje-jeniyoyin da bangarorin 2 suka cimma a zaman dasukayi jiya Alhamis.

SSANU da NASU za su tsunduma yajin aikin makwanni biyu

Ba za mu dena yajin aiki ba sai gwamnati ta biya mana bukatun mu – ASUU

Ministan kwadago na kasar Chris Ngige, ya bayyana kwarin gwiwa kan yuwar Janye yajin aikin.

Anasa bangaren shugaban kungiyar malaman jami’o’in Najeriyar Biyodin Ogunyemi, yace akwai bukatar jama’a su kalli matsalolin da jami’o’in kasar ke fuskanta da idon basira domin yin wani abu akai.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!