Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta ayyana juma’a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun bikin Maulidi

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana Juma’a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutu domin bikin Maulidi na tunawa da ranar haihuwar annabi Muhammad (S.A.W).

Gwamnatin ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin cikin gida ta ƙasar ta fitar ranar Laraba, wadda ta samu sa hannun babbar sakatariya a ma’ikatar, Magdalene Ajani.

Miliyoyin al’ummar Musulmi ne ke bukukuwan Maulidi a Najeriya da kuma faɗin duniya a duk irin wannan lokaci, kowace shekara.

Sanarwar da gwamnatin Najeriyar ta fitar ta buƙaci al’ummar ƙasar su yi amfani da lokacin wajen yin addu’o’in samun zaman lafiya a ƙasar, wadda ke fama da matsaloli na tsaro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!