Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya ta bayar da hutun bikin ranar samun yanci

Published

on

Gwamnatin tarayya  ta ayyana  gobe Laraba a matsayin ranar hutu a fadin  ƙasar domin bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ƴancin kai.

 

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da ministan cikin gida Olibunmi Tunji-Ojo ya fitar, wadda a cikinta ya taya ƴan Najeriya murnar cimma wannan babban matsayi.

 

Ministan ya kuma buƙaci ƴan ƙasar su ci gaba da nuna kishin ƙasa da hadin kai da juriya, da ya ce su  ke taimaka wa ƙasar wajen dunƙulewa waje guda ga mabanbantan kabilun ta  tun lokacin samun ƴancin kai a 1960.

 

A ranar 1 ga watan Otoban 1960 ne dai Najeriya ta samu ƴancin kai daga Turawan mulkin Birtaniya da suka yi mata mulkin mallaka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!