Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta bukaci rufe asusun ajiyan banki guda biyar mallakin babban jojin kasa

Published

on

Gwamnatin tarayya ta bukaci sashen kula da hada-hadar kudi ta kasa NFIU da ya rufe asusun ajiyan banki guda biyar mallakin babban jojin kasa Walter Samuel Onnoghen.

Attorney janar na kasa kuma ministan shari’a Abubakar Malami ne ya ba da wannan umarni.

A cikin wata wasika mai dauke da sa hannun wani makusancin Attorney janar na kasa mai suna Abiodun Aikomo ta bukaci da a rufe asusun ajiyan har sai an kammala shari’ar da a ke yi ma sa a kotun da’ar ma’aikata.

A baya-bayan Nan ne dai aka gurfanar da babban jojin kasa Walter Samuel Onnoghen gaban kotu kan zargin sa da mallakar wasu asusun ajiya na banki guda biyar, wanda tun farko bai bayyana su cikin kadarorin da ya mallaka ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!