Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta ce dakarun sojin kasar nan za su shiga cikin tsarin Inshorar Lafiya ta kasa

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce dakarun sojin kasar nan za su shiga cikin tsarin Inshorar Lafiya ta kasa, domin tabbatar da cikakkiyar kulawa da lafiya ga jami’an tsaro, iyalan su da kuma waɗan da suka yi ritaya.

Karamin Ministan tsaro Bello Matawalle ne ya bayyana hakan a Abuja a jiya Talata, yayin bikin cika shekaru 20 da haɗin gwiwar shirin kiwon lafiyar ma’aikatar tsaro da Walter Reed Army Institute of Research Africa.

Matawalle ya ce wannan mataki zai karfafa tsarin kiwon lafiyar rundunar tsaro ta kasa tare da tabbatar da cewa dakarun soji da iyalan su suna samun irin kariyar lafiyar da sauran ‘yan kasa ke samu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!