Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta sha alwashin kammala aikin titin Wuju-wuju shekaru 2

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce, za ta kammala aikin titin Wuju-wuju cikin watanni 24.

Ƙaramin ministan ayyuka da gidaje, Yusuf Abdullahi Ata, ne ya bayar da wannan tabbaci bayan ƙaddamar da aikin titin a ranar Litinin.

Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta ware Naira Biliyan Arba’in da Bakwai don ganin an kammala titin wanda tsohon gwamna Kwankwaso ya fara yin shi a lokacin da ya ke kan mulki.

Haka kuma, Yusuf Ata ya ce, ya musanta Rahotonnin da ke cewa aikin haɗin gwiwa ne da Gwamnatin jihar Kano.

Ministan, ya kuma bayar da tabbacin ci gaba da biyan diyyar waɗanda aikin ya shafa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!