Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

A ƙara haƙuri kan aikin titin Kano zuwa Abuja – Buhari

Published

on

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya aiko tawaga ta musamman domin tattaunawa kan aikin titin Kano zuwa Abuja.

Tawagar na bisa jagorancin shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa Farfesa Ibrahim Gambari.

Yayin duba aikin a jihar Kaduna Gambari ya ce, duba da muhimmancin da aikin, ya sanya shugaban ƙasa ya turo ayarin domin duba yadda aikin ke tafiya.

A cewarsa, matsalar da turakun wuta na cikin abin da ke kawo tsaiko a aikin.

Saboda haka ya roƙi al’umma su ci gaba haƙuri har zuwa kammala aikin.

Hoto a yayin taron.

A jawabinsa Gwamna Abdullahi Ganduje ya ce, ya bayyana gamsuwarsa kan yadda aikin ke gudana.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayin da ya ke jawabi a wurin taron.

Daga cikin waɗanda ke cikin tawagar sun haɗa da, ministan ayyuka da gidaje Babatunde Fashola.

Da kuma ministar kuɗi Zainab Shamsuna Ahmad.

Labarai masu alaka:

Shamsu Kura ya kalubalanci Buhari kan aikin titin Kano zuwa Abuja

Ƴan majalisa na duba ayyukan gwamnatin tarayya a Kano

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!