Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya za ta fara yin gwajin tu’ammali da ƙwaya ga wadanda za ta dauka aiki

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya, ta ce, za ta ɓullo da shirin yin gwajin miyagun ƙwayoyi ga masu neman aikin gwamnati, ta na mai cewa, daga yanzu za a saka gwajin ta’ammali da ƙwaya a cikin abubuwan da suka zama dole kafin a ɗauki mutum aiki.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayya, Segun Imohiosen ya fitar.

Sanarwar ta ƙara da cewa hukumomin ƙasar nan za su haɗa hannu da hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi wato NDLEA ne domin samun nasarar wannan aikin.

Ya ƙara da cewa ɗaukar wannan matakin ya zama dole ne bayan yawaitar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi, musamman a tsakanin matasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!