Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya zata baiwa jihohi kudaden Paris club

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce nan bada dadewa ba, za ta bai wa jihohi kason karshe na kudaden Paris Club da ya kai sama da naira biliyan dari shida da arba’in da tara.

Ministan kudi Zainab Ahmed ce ta bayyana haka yayin wani taron manema labarai jiya a Abuja

Ta ce tuni ma’aikatar kudi ta kammala aikin tantance kididdigar sauran kudaden da ya rage domin mayar da shi ga jihohi.

Da ta ke magana kan kasafin kudi kuwa, ministar cewa ta yi, tsakanin watan Yunin bara lokacin da shugaban kasa ya sa hannu kan kasafin kudin shekarar da ta gabata zuwa watan Mayun bana gwamnatin tarayya ta fitar da sama da naira tiriliyan biyu don gudanar da manyan ayyukan raya kasa a sassa daban-daban na kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!