Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Majalisar zartarwa ta amince da kashe biliyan 27 a ayyukan raya kasa

Published

on

 

Majalisa zartaswa  ta amince da fitar da Naira Billiyan 27 don sayan buhu-hunan Gero da kayayaykin wuta lantarki da kuma gyara wasu daga cikin Titunan Birnin tarayya Abuja.

Ministan Noma da albarkatun kasa Audu Ogbeh ne ya bayyana haka, a zaman majalisar na jiya, wanda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.

Audu Ogbeh  ya kuma ce, an ware Naira Billiyan Tara da milliyon hudu da nufin sayan Gero tan Dubu sittin  baya ga amince da sayan tan din Masara Dubu sitin da daya da Dawa da kuma Ridi, don samar da iri da za a suka a damar bana.

A nasa banagaren Ministan wutan lantarki da gidaje   Babatunde Raji Fashola ya ce majalisar ta kuma amince da fitar da Naira Biiliyon Bakwai da Milliyon daya, don gyara titin Abaji mai hannu biyu da wata gada, duk a  birnin tarraya Abuja don saukaka masu ababen-hawa zirga-zirga.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!