Connect with us

Labarai

Gwamnonin Arewa maso gabas sun buƙaci shugaba Tinubu ya fifita aikin haƙar fetur a yankin

Published

on

Gwamnonin yankin arewa maso gabashin kasar nan sun buƙaci shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya fifita komawa aikin haƙar man fetur a rijiyoyin Kolmani da na yankin tafkin Chadi a wani ɓangare na yunƙurin farfaɗo da tattalin arziki da rage matsalar tsaron yankin.

 

Gwamnonin sun bayyana hakan ne a lokacin da suka ziyarci shugaba Tinubu a fadar mulki ta Villa da ke birnin tarayya Abuja.

 

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, wanda ya yi magana a madadin gwamnonin, ya ce komawa aikin haƙar man yankin zai taimaka wa ayyukan soji a yankin tare da buɗe ƙofar ayyukan ci gaba a yankin.

 

Zulum ya yaba wa Shugaba Tinubu kan ci gaba da yaƙi da Boko Haram tare da bayar da tallafi ga iftila’in ambaliya da ya auku a jiharsa a shekarar da ta gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!