Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnonin arewa sun yiwa gwamnan jihar Kwara ta’aziyyar rashin mahaifinsa

Published

on

Kungiyar gwamnonin arewacin kasar nan sun nuna alhinin bisa rasuwar mahaifin gwamnan jihar Kwara Abdurrahman Abdurrazak wato Alhaji Abdulganiyyu Folorunsho Abdurrazak mai darajar SAN wanda ya rasu a daren Asabar.

Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Plateau Simon Lalong ne ya aike da ta’aziyyar ta hannun daraktan yada labarai na kungiyar Dakta Makut Macham a yau Asabar.

Sanarwar ta bayyana rasuwar Alhaji Abdulganiyyu Abdaurrazak a matsayin rashi babba a kasar nan kasancewar sa mutum na farko a arewa da ya taba zama lauya kuma mai lambar kwarewa ta SAN a don haka babban rashi ne ga al’ummar jihar Kwara da ma kasa baki daya.

Kazalika sanarwar ta bayyana marigayin a matsayin wanda ya sadaukar da rayuwar sa wajen hidimtawa al’umma a lokacin rayuwar sa wanda baza a manta da rashin sa ba tsawon rayuwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!