Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Hakuri shi ke inganta zamantakewar aure – Sheik Ali Yunus

Published

on

Limamin masallacin Juma‘a na Usman bin Affan dake Gadon Kaya Sheik Ali Yunus ya ce, babban abunda ke taka rawa wajan inganta aure shi ne hakuri da juriya, baya ga inganta zamantakewar juna.

Limamin ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan gidan Rediyo Freedom da ya gudana a yau, yana mai cewa, mafi yawan lokuta abunda da ke janyo lalacewar aure shi ne, rashin kai zuyciya nesa da wasu daga cikin ma’auratan ke yi.

Malamin ya kuma ce, rashin ilimin zamantakewar aure shi ma yana taka rawa wajen lalacewar auren wannan lokacin
Sheik Ali ya kuma ce, kamata ma’aurata su daina zargin junan su, sannan su rubanya kokarin sun a son kyutatawa juna.

Limami ya kuma yi kira ga ma’aurata da su rungumi dabi’ar yin hakuri da juriya don kaucewa bacin rana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!