Labarai
Halin da โyan gudun hijira ke ciki a fadin duniya

Hukumar โyan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce kusan rabin โyan gudun hijira a fadin Duniya yara ne kanana.
majalisar na bayyana hakan ne a shafinta na Twitter a wani bangare na bikin tunawa da ranar โyan gudun hijira.
Nearly half of all refugees are children.
๐ง๐พ๐ถ๐ป๐ง๐ฝ๐ง๐ป๐ถ๐ผ๐ฉ๐พ๐ง๐ป๐ฆ๐ฟ๐ฉ๐พโ๐ฆฑ๐ฉ๐ผโ๐ฆฐ๐ถ๐พ๐ง๐ฟ๐ฆ๐ฝ๐ง๐ฟ๐ง๐พ๐ฑ๐ผโโ๏ธ๐ฆ๐พ๐ง๐ฝ pic.twitter.com/2vYEy8WkL7โ UNHCR, the UN Refugee Agency (@Refugees) June 20, 2020
Wani rahoto da hukumar ta fitar abu na farko, ya nuna cewa akwai mutane miliyan 70.8 a fadin duniya da yake-yake ya tilastawa barin muhallansu, wanda ta ce ya zarce na mutanen da yakin duniya na biyu ya daidaita.
Abu na biyu shine, daga cikin wadanda yaki ya tilastawa barin gidajensu, akwai โyan gudun hijira miliyan 25.9, akwai kuma miliyan 41.3 da ke gudun hijira a kasashensu, sai kuma masu neman mafaka da ke jiran a basu takardar shaidar gudun hijira a wasu kasashen su miliyan 3.5.
Abu na uku ya nuna cewa sama da rabin โyan gudun hijira miliyan 25.9 da ake da su a fadin duniya yara ne โyan kasa da shekara 18.
A cewar hukumar UNHCR abu na hudu shine ya zuwa watan Mayu 2020, akwai masu neman mafaka miliyan 2.2 daga kasar Sudan ta Kudu kadai.
A kowacce dakika akan tilastawa mutum guda barin muhallinsa saboda rikice-rikice.
Kimanin kashi 25 cikin 100 na mutanen da suka rasa muhallinsu mata ne, inda kashi hudu daga cikin su mata ne masu juna biyu.
Kusan kashi 70 cikin 100 na โyan gudun hijira na rayuwa ne cikin tsananin talauci.
Kasashe masu tasowa na da kaso 80 na โyan gudun hijirar da suka tserewa yake-yake.
ย
You must be logged in to post a comment Login