Connect with us

Labarai

Hare-haren Boko Haram ne ya hana Jonathan cire tallafin mai – Sarki Sunusi II

Published

on

Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi II kuma tsoho gwamnan Babban Bankin kasa CBN, ya bayyana cewa tsoron hare-haren Boko Haram ne ya sa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya dakatar da shirin cire tallafin man fetur a shekarar 2012.

‎Yayin da yake jawabi a Abuja ranar Talata, a taron Oxford Global Think Tank Leadership da ƙaddamar da wani littafi, Sanusi ya ce ba zanga-zangar jama’a ba ce ta sanya gwamnatin Jonathan ta ja da baya, sai dai bayanan sirri da gwamnati ta samu kan yiwuwar kai hare-hare a wuraren da masu zanga-zanga suka taru.

A cewar Sarkin, gwamnatin wancan lokaci ta fi mayar da hankali wajen kare rayukan ‘yan kasa, musamman ganin cewa kungiyar Boko Haram na cikin mafi girman tashin hankali a Arewa maso Gabas a lokacin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!