Connect with us

Ƙetare

Harin da Iran ta kai a Tel Aviv ya jikkata mutum 14

Published

on

Rahotanni daga hukumomin Isra’ila sun ce wani hari da Iran ta kai da makami mai linzami a Tel Aviv a yau ya jikkata mutum 14..

 

Ba a samu rahoton cewa harin ya lalata wurare ba lalacewa amma hukumomin agajin gaggawa na Isra’ila sun ce mutum goma sha huɗu sun jikkata sakamakon hare-haren a unguwannin da ke kusa da Tel Aviv.

 

A safiyar yau, an yi kira ga mazauna wasu yankuna a tsakiyar Isra’ila, ciki har da Tel Aviv, su nemi mafaka sau da dama.

 

Hukumomin Isra’ila sun ce mutum 19 ne suka mutu tun farkon rikicin, mafi yawansu sakamakon ƙananan ɓirɓishin makaman masu linzami da aka kakkaɓo

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!