Connect with us

Labarai

Harin Masallaci a Borno ya hallaka mutane 5

Published

on

Wani mummunan tashin bam ya auku a wani masallaci dake kasuwar Gamboru a cikin birnin Maiduguri, babban birnin jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya.

Lamarin ya faru ne a yammacin jiya laraba, inda har yanzu ba a tabbatar da adadin waɗanda suka rasu ko suka jikkata ba, sai dai rahotanni na nuna cewa mutane da dama ne suka jikkata ko suka rasa rayukansu.

Rahotanni sun ce tune  an garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitoci daban-daban domin samun kulawar gaggawa, yayin da jami’an tsaro suka kasance a wajen.

Sai dai daga bisani gwamnatin jihar ta fitar da rahoton cewa, mutane 5 ne suka rasu sakamakon harin, yayin da 35 kuma suka jikkata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!