Connect with us

Labarai

Harin NDA: Akwai rauni a harkar tsaron Najeriya – ACF

Published

on

Ƙungiyar dattawan Arewa ta ce mamayar da yan bindiga suka yiwa kwalejin koyar da harkokin tsaron Najeriya ya nuna cewa tsaron kasar yana da rauni.

Sakataren yaɗa labaran Kungiyar Emmanuel Yawe ne ya sanar da hakan, ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta ce, rashin tsaro ne ya sanya a kwanakin baya wasu da ba a san ko suwaye ba, suka harbo jirgin yakin sojojin Najeriya, sai kuma aka gano yadda yan bindga suka lalata kwalejin NDA ta hanyar kai musu hari.

A cewar sanarwar wannan ya nuna ƙarara Najeriya ta gaza wajen sha’anin tsaro.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!