Connect with us

Labarai

NEMA ta jagoranci aikin ceto bayan ambaliyar ruwa data afkawa ƙauyuka 13 a Adamawa

Published

on

Hukumar ba da agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) reshen Yola da ke jihar Adamawa ta jagoranci aikin ceto bayan ambaliyar ruwa data afkawa ƙauyuka 13, da ke cikin ƙananan hukumomin Jihar.

Shugaban ayyukan hukumar ta NEMA a Yola, Ladan Ayuba, ya ce tawagar gaggawa daga hukumar tare da hadin gwiwa da ta jihar ADSEMA, da jami’an kashe gobara na jiha da na tarayya tare da masu aikin sa-kai sun shiga yankunan domin ceto jama’ar da ambaliyar ta rutsa da su.

Ladan Ayuba ya kara da cewa an kwashe mata da yara da tsofaffi da masu nakasa daga yankunan da ke cikin haɗari zuwa sansanonin wucin-gadi da wuraren da suka dace. Inda kuma ake cigaba da bincike don gano girman illar ambaliyar, da asarar dukiya da gine-gine da aka samu, da kuma duba agajin da ake bukata a yankunan.

Sai dai kuma ya tabbatar da cewa, babu wanda ya rasa ransa sakamakon ambaliyar ruw

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!