Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Hukumar bincike kan hadarin jiragen sama ta fitar da rahoto kan jirgin da ya fadi a Legas

Published

on

Hukumar bincike game da aukuwar hadarin jiragen sama ta kasa AIB ta fitar da kwarya-kwaryar rahoton farko na hatsarin jirgi mai saukar Ungulu da ya fada kan wani gini a yankin Opebi da ke Jihar Lagos a ranar 28 ga watan Agustan jiya.

Rahoton ya bayyana cewa karewar man jirgin ce ta haddasa hatsarin.

Jirgin dai ya tashi ne daga garin Fatakwal na Jihar Rivers da karfe 9:20 na safiyar ranar, wanda ake sa ran saukarsa a Lagos da sa’o’i biyu da minti 40 bayan tashinsa, amma kuma ya fada kan wani gini da karfe 12:14 na rana.

Haka zalika binciken ya gano cewa wa’adin sakamakon gwajin lafiyar matukin jirgin ya kare tun a ranar 6 ga watan Agustan da ya gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!