Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar EFCC zata daukaka kara kan batun rufe asusun gwamnatin jihar Benue

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasa EFCC zata dauka ka karar kan hukuncin da babbar kotun tarayya na rufe asusun gwamnatin jihar Benue.

Wannan na kunshe cikin sanarwar da mai Magana da yawon hukumar ta EFCC Tony Orilade ya fitar cewa hukuncin da mai shari’a Mobolaji Olajuwon ya yanke a babbanr kotun dake birnin Makurdi ta jihar Beneu wace gwamnatin jihar ta nemi hukumar EFCC ta biya ta kudin diyya na bata mata suna na Naira miliyan 50 da kuma wasu bankunan kasuwanci guda 2 suma su biya Naira miliyan 25.

A dai watan Agustan bara ne sashin bincike na hukumar EFCC  ya bada umarnin da a rufe asusun kudi na gwamnatin jihar na wucin gadi.

Sai dai mai Magana da yawon hukumar ta EFCC ya ce lauyoyin hukumar na yi duk mai yuwa wajen daukaka kara don kalubalantar hukuncin da kotun ta yanke.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!