Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar habaka harkokin kimiyya ta kasa ta ce akwai yiwuwar matsalar kutse a wannan shekara

Published

on

Hukumar habaka harkokin kimiyya da fasaha ta kasa NITDA ta bukaci hukumomi da ma’aikatun gwamnati, hadi da bangarori masu zaman kan su do su yi taka tsan-tsan game da matsalar masu kutse cikin wannan shekarar.

Shugaban hukumar na kasa Dakta Isah Pantami ne ya bayyana hakan lokacin da suke zantawa da manema labarai yau a birnin tarayya Abuja.

Dakta Pantami ya kuma bayyana cewa bankuna, da ma’aikatun lafiya, bangaren bayar da hasken lantarki hadi da bangarorin samar da ababen more rayuwa, hadi da wasu bangarori daban-daban ne ake fargabar masu kutsen zasu iya yiwa danyan aiki.

A cewar sa akwai wani sashen bayar da agajin gaggawa ga wadanda suka fuskanci matsalar kutse da hukumar ta ware tare da hadin gwiwar masu ruwa da tsaki a bangaren kimiyya, duk da nufin dakile ayyukan na su.

Shugaban hukumar ya ce yanzu haka hukumar ta daura damarar fuskantar duk wani kalubale daga bangaren masu kutsen, kuma ba zatayi kasa a gwiwa ba wajen dakile ayyukan su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!