Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar INEC ta karyata zargin jam’iyyun siyasa na shrine daukar ma’aikatan N-Power

Published

on

A wani labarin kuma Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta karyata zargin da ganayyar jam’iyyun siyasa suka yi mata na  cewa tana shirin daukar ma’aikatan N-POWER a matsayin ma’aikatan wucin gadi.

Daraktan katin zabe da wayar da kan jama’a na hukumar ta INEC Mr, Oluwole Osaze-uzi bayyana hakan cikin sanarwar da ya fitar cewa hukumar zabe  na daukar masu bautar kasa ma’aikatan wucin gadi don gudanar da zabe.

Mr, Oluwole Osaze-Uzi ya kara da cewar, sai dai in sami gibi ne, zai sanya ta yi amfani da daliban manyan makarantu, ko kuma tsofafin masu bautar kasa, amma babu wani shiri na amfani da ma’aikatan da suka ci gajiyar shirin na N-POWER.

Kuma kowa yasan cewar, tun bayan da aka  kafa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC na amfani da masu bautar kasa wajen gudanar da zabe a matsayin ma’aikatan wucin gadi, kuma bayar da za’a yi kwatsam wannan gwamnati ta sauya wancen tsari.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!