Connect with us

Kiwon Lafiya

Hukumar kula da da’ar ma’aikata ta sammaci babban sakataren a ma’aikatar lantarki ayyuka da gidaje

Published

on

Hukumar kula da da’ar ma’aikata ta kasa ta yi sammacin babban Sakatare a ma’aikatar Lantarki ayyuka da gidaje Mista Louis Edozien domin gurfana gabanta tare da amsa tambayoyi almundahana.

Rahotanni sun bayyana cewa cewa Mista Louis Edozien zai gurfana a Sakatariyar hukumar da ke birnin tarayya Abuja a yau Laraba.

Gayyatar dai ta biyo bayan takardar korafi da wata tsohuwar babbar Manajar kamfanin samar da wutar lantarki na Neja-Delta Maryam Muhammad ta rubatawa hukumar ana zargin babban Sakataren da rashincancantar mukamin na sa, baya ga son rai da ya rika sanyawa cikin aikin.

Mista Edozien wanda shi ma ya taba rike mukamin babban manajan kamfanin samar da lantarkin na Neja-Delta, ya zamanto cikin manyan Sakatarori 18 da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada a cikin wtan Nuwamban shekarar 2015.

Maryam Muhammad ta shaidawa hukumar kula da da’ar ma’aikatan cewa a baya can an kori Mista Louis Edodien daga aiki a kamfanin sakamakon gaza gabatar da ingantacciyar shaidar aikin bautar kasa wato NYSC ceritificate, bayan dogon bincike.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!