Labarai
Buhari zai raba mitar wutar lantarki miliyan 36 cikin watanni uku masu zuwa
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/03/Prepaid-Meter.jpg)
Hukumar kula da bangaren samar da wutar lantarki ta kasa, ta ce, nan da watanni uku masu zuwa, za a sanyawa gidaje akalla miliyan talatin da shida mitar wutar lantarki a fadin kasar nan baki daya.
A cewar hukumar shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya ba da wannan umarni.
Karamin ministan samar da wutar lantarki, Goddu Jedy-Agba ne ya bayyana haka a jiya juma’a, jim kadan bayan duba aiki a wani kamfanin gwajin na’urar mitar lantarki a jihar Enugu.
Ya ce nan da makwanni shida masu zuwa ne ake sa ran za a kaddamar da kamfanin gwajin mitar.
A cewar sa manufar kafa kamfanin gwajin mitar ita ce, tabbatar da cewa duk mitoci da za a shigo da su kasar nan sun cika duk ka’idoji da ake bukata.
You must be logged in to post a comment Login