Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar Naptip ta kama wasu mutane 8 da zargin safarar mutane

Published

on

Hukumar yaki da safarar mutane ta kasa NAPTIP ta ce ta kama wasu mutane takwas da ake zargin masu safarar mutane ne.

 

Shugaban hukumar da ke kula da shiyyar garin Benin Mista Nduka Nwanwenne shi ne ya shaidawa manema labarai hakan a yau Laraba a garin Benin da ke jihar Edo inda ya ce an kama wadanda ake zargin ne watanni uku da suka gabata.

 

A cewar sa hukumar ta kubutar da akalla mutane 138 da aka yi safarar su a tsakanin lokacin da aka kama su inda kuma wasu 124 daga cikin wadanda aka kubutar suka koma ga dangin su.

 

Shugaban ya kuma ce  kawo yan zu batutuwan harkar safarar mutane da ke gaban kotuna daban daban a kasar nan sun kai tamanin da tara.

 

Ya kuma ce sun samu rahotannin safarar mutane har 34 daga korafin da ake aikewa hukumar daga dai-daikun mutane, inda kuma ta samu rahoton wasu goma sha hudu daga hannun jami’an tsaro.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!