Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar NDLEA ta kama wani mutum da ake zargin da safaran makamai jihar Benue

Published

on

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta kama wani mutum da ake zargi da Safaran Bindigogi zuwa Jihar Benue.

Mataimakin kwamandan hukumar a Jihar Jigawa Oko Michael ne ya tabbatar da hakan yana mai cewa jami’ansu ne suka kama mutumin a ranar Lahadin da ta gabata a yayin da su ke aikin sintiri a kan hanyar Jahun zuwa Gujungu.

Mutumin mai suna Salisu Mamuda da suka ce dan asalin Jihar Kaduna ne, ya yi karatunsa ne a Jihar Nassarawa inda kuma ya ke aikin safarar karafunan da suka lalace daga Jihar ta Nassarawa zuwa Benue.

Salisu Mamuda, ya ce wasu mutane daga Jihar Benue ne suka bukaci ya kai musu Bindigogin ta hanyar amfani da wani abokinsa.

Hukumar ta NDLEA ta ce za ta mika mutumin tare makaman da aka samu a hannunsa zuwa hannun ‘yan-sanda a Jihar ta Jigawa domin fadada bincike.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!