Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar yan sanda ta kame a kalla mutans 145 bisa zargin tashe-tashen hankulan jihar Benue

Published

on

Akalla mutane 145 Rundunar ‘yan-sanda ta cafke bisa zarginsu da hannu cikin tashin hankalin da ke faruwa a Jihar Benue, inda aka gurfanar da 124 daga cikinsu gaban kuliya.

Goma sha shida daga cikinsu an zarge su da hannu cikin rikicin da ya yi sanadiyar mutuwar wasu Fulani 7 a garin Gboko na Jihar ta Benue a ranar 31 ga watan jiya.

Wadannan bayanai na kunshe cikin kunshin bayan da babban Sufeton ‘yan-sandan kasar Ibrahim Idris ya gabatarwa kwamitin hadin gwiwa kan harkokin tsaro na Majalisar Dattijai a ranar Juma’ar da ta gabata.

Gwamnan Jihar ta Benue Samuel Ortom y adage dokar hana zirga-zirgar da ya sanya a garin Gboko, kamar yadda mashawarcin gwamnan na musamman kan harkokin yada labarai Tahav Agerzua ya sanar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!