Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ministan Ilmi Adamu Adamu ya fara zagayen cibiyoyin da aka ware don gudanar da jarrabawar JAMB

Published

on

Ministan Ilmi na Najeriya Malam Adamu Adamu ya fara zagayen duba cibiyoyin da aka ware don gudanar da jarrabawar shiga manyan makarantun ta JAMB ta shekarar da muke ciki.

Lokacin da ya kai ziyarar gani da ido cibiyoyin Digital Bridge da Global Distance Learning a Abuja juma’ar nan, Malam Adamu ya bayyana wa manema labarai gamsuwar sa da iri shirin da cibiyoyin suka yi.

Ministan ilmin ya kuma yi kira ga daliban da za su zauna jarrabawar da su kara dagewa wajen koyon kwamfuyuta domin hakan zai taimaka musu wajen gudanar da jarrabawar yadda ya kamata.

Malam Adamu Adamu ya kara da cewa babu bukatar a samawa dalibai mataimaka yayin jarrabawar matukar daliban sun iya kwamfuyuta, kuma hakan zai taimaka musu gaya wajen gudanar da jarrabawar cikin sauki.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!