Labarai
Hukumar NEMA ta sanar da adadin mutanen da suka rasu sakamakon tashin Bomb a Maiduguri

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya NEMA ta ce akalla mutane 23 ne suka rasa ransu, sakamakon tashin Bomb da aka samu a Maidugurin jihar Borno.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, shugaban hukumar a jihar Surajo Abdullahi, ne ya tabbatar Mata da hakan.
Ya kuma ce, mutane 146 ne suka samu raunuka inda yanzu haka suke Asibiti dan karbar kulawar likitoci.
You must be logged in to post a comment Login