Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar NIMC zata koma kar kashin kulawar ma’aikatar sadarwa – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da mayar da hukumar yi wa ‘yan kasa rijista ta NIMC zuwa ma’aikatar sadarwa ta zamani a birnin tarraya Abuja.

Hakan na cikin wata sanarwar mai dauke da sa hannun mai magana da yawun ma’aikatar sadarwa Uwa Sulaiman.

Sanarwar ta bayyana cewa, amincewar mayar da hukumar ta NIMC zuwa ma’aikatar sadarwa ya biyo bayan la’akari da gwamnati ta yi da irin rawar da za ta bayar na samar da dabarun bunkasa harkokin sadarwar zamani.

Sanarwar ta kara da cewa, mayar da hukumar wajen zai taimaka wajen ganin an samu daidaito tsakanin ma’aikatar sadarwa da hukumar NIMC don ba ta damar bibiyar yadda za a samar da hanyoyin sadarwa masu mahimmanci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!