Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Hukumar WAEC Ta Fitar Da Sakamakon Jarabawar 2023

Published

on

Hukumar shirya jarrabawar Afrika ta yamma WAEC, ta fitar da sakamakon jarabawar kammala makarantun sakandare ta yammacin Afrika ta 2023 (WASSCE).

 

Shugaban hukumar Patrick Areghan, shugaban ofishin Najeriya (HNO) na WAEC, a yammacin Litinin din nan ya ce daga cikin mutane 1,613,733 da suka zana jarabawar, an hana sakamakon Ɗalibai 262,803 “saboda rahotannin da aka samu na magudin jarabawar.

 

Ya ce an samu ci gaba a fannin samun gurbin karatu a matsayin jimillan mutane 1,361,608, masu wakiltar kashi 84.38 cikin 100, sun samu kiredit da sama da haka a mafi karancin darussa biyar masu dauke da harshen Ingilishi ko lissafi.

 

Haka kuma, Ɗalibai 1,287,920, wadanda ke wakiltar kashi 79.81 cikin 100 na jimlarsu, sun samu kiredit da sama da haka a cikin mafi karancin darussa biyar, da suka hada da Ingilishi da Lissafi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!