Labarai
WAEC ta rike sakamakon dalibai 167,486 bisa zargin satar jarrabawa

Hukumar shirya jarabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka WAEC, ta rike sakamakon dalibai 167,486, wanda ya kai kasho 8.59 cikin 100 na wadanda suka rubuta Jarabawar ta bana 2026 da aka gudanar ta hanyar amfani da na’ura mai kwakwalwa CBT, bisa zargin aikata magudin jarrabawa.
Shugaban ofishin WAEC na Najeriya Dakta Amos Dangut ne ya bayyana hakan yayin da yake sanar da fitar da sakamakon jarabawar a birnin Legas yau Laraba.
Dangut ya ce, an rike sakamakon daliban ne saboda laifuka daban-daban da suka hada da yawaitar amfani da wayoyin hannu a dakunan jarabawa duk da haramcin hakan, da kuma shirya magudin jarabawa a wasu makaran tu.
You must be logged in to post a comment Login