Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Hukumar zaɓe ta kano ta sanya ranar zaɓen ƙananan hukumomi

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Kano ta ce zata gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi 44 dake faɗin jihar a ranar 30 ga watan Nuwamban shekarar 2024 domin bawa ƙananan hukumomi damar cin gashin kan su da kotu ta bayar da umarni.

Shugaban hukumar Farfesa Sani lawan Malumfashi ne ya bayyana hakan da safiyar yau yayin taron manema labarai da ya gudana a ofishin hukumar.

Farfesa Malumfashi ya kuma tabbatar da cewa za’a ko wace jam’iyya da take shirin yin takara, za’a fara yakin neman zaɓen a ranar 1 ga watan Nuwambar.

Haka kuma shugaban hukumar ya tabbatar da cewa duk wani ɗan takara da aka samu da sanya fastar sa a gidan gwamnati ko masarauta zata sauke shi daga jerin ƴan takara.

Hukumar ta ce zata fara shirye-shiryen fara gudanar da zaɓen a ranar 15 ga watan Agusta inda shugaban hukumar yace za’a gudanar da zaɓe cikin gaskiya da nufin ayyana duk wanda ya sami nasarar lashe zaben.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!