Labarai
ICPC ta kara tsare Nasir El-Rufa’i

Hukumar yaƙi da cin hanci ta ICPC ta sake kama tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa’i, bayan da aka kasa kammala sauraron buƙatar belinsa a kotun tarayya da ke Kaduna. Alkalin kotun, Mai shari’a Rilwan Aikawa, ya ɗage shari’ar zuwa ranar Laraba domin ci gaba da sauraron bukatar.
Jinkirin ya biyo bayan sabbin muhawara da ƙorafe-ƙorafe tsakanin ɓangaren masu gabatar da ƙara da kuma lauyoyin El-Rufai.
Tun da fari, ɓangaren tsaro ya nemi alkalin ya janye kansa daga shari’ar bisa zargin son rai, amma daga bisani suka janye wannan buƙata, lamarin da ya haddasa tsaiko a shari’ar.
Ana tuhumar El-Rufai da laifuffuka da suka haɗa da karkatar da dukiyar jama’a da sauran al’mundahar kuɗi, ciki har da zargin karɓar sama da Naira miliyan 289 a matsayin alawus da ya zarce haƙƙinsa, da kuma kusan dala dubu 797 da ake zargin kudin haram ne.
Bayan zaman kotun, jami’an ICPC suka kara tsare shi, yayin da aka tsaurara tsaro a harabar kotun tare da hana ‘yan jarida shiga.
You must be logged in to post a comment Login