Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ikon Allah: Wata mata ta haifi ‘ya’ya 9 rigis

Published

on

Rahotanni sun ce a ranar talata ne Halima Cisse – mai shekara 25 ta haifi jariran nata

 

Jariran dai sun kunshi mata biyar da maza huɗu a wani asibiti da ke kasar Morocco

 

Kamar yadda ministan lafiyan kasar ta Mali Fanta Siby ta fitar ta cikin wata sanarwa.

 

Tun farko dai an sa ran Ms Cisse za ta haifi ƴaƴa bakwai ne bisa ga hoton cikinta da aka ɗauka a Mali da Morocco wanda bai iya gano cewa akwai karin jarirai biyu ba a cikinta.

 

Dr Siby ta ce jariran da mahaifiyarsu na cikin “ƙoshin lafiya”. Ana kuma sa ran za su koma gida nan da wasu makwanni.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!