Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sabuwar dokar cirar kudi a Nijeriya zata taimaka wajen inganta tattalin arzikin ta-Dakta Kani

Published

on

Wani masanin tattalin arziki da ke kwalejin Sa’adatu Rimi a nan Kano, Dakta Abdulsalam Muhammad Kani ya ce, dokar takaita cirar kudade a bankuna da babban bankin kasa CBN ya fito da ita, za ta taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya.

Dakta Abdussalam Kani ya bayyana haka ne a zantawarsa da Freedom Radio

Dakta Abdussalam Kani ya kara da cewa, sabuwar dokar bankunan zata kawar da barazanar rike manyan kudade a hannun al’umma ko ajiye su a gida, tare da gudanar da hada-hadar kudade cikin sauki.

Ya kuma ce dokar zata taimaka wajen hana satar kudaden gwamnati da kuma yaki da ayyukan ta’addaci a Najeriya.

Don haka yake shawartar al’umma dasu rungumi wannan tsarin na ajiyar kudi a bankuna, don gujewa matsalolin da aka iya zuwa, su dawo.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!