Connect with us

Labarai

Ina daga cikin mutanen da masu shirin juyin mulki ke son kamawa- Ministan Tsaro

Published

on

Ministan Tsaron ƙasar nan Janar Christopher Musa mai ritaya, ya bayyana cewa yana daga cikin mutanen da masu shirin juyin mulki suka sa a jerin waɗanda za a kama ko a hallaka idan suka ƙi bin umarni su.

 

Christopher Musa ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels, bayan rundunar soji ta tabbatar da cewa an bankado yunkurin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

 

Janar Christopher Musa ya ƙara da cewa shi kansa an shirya kama shi, kuma idan ya ƙi, za a kashe shi, inda Ya ƙara da cewa wasu manyan jami’an gwamnati suma na cikin jerin mutanen da aka yi niyyar hallakawa.

 

Sai dai Tun a watan Oktoba ne aka kama wasu sojoji daga matakin Kyaftin zuwa Birgediya-Janar bisa zargin shirya juyin mulki.

 

Inda Rahotanni suka nuna cewa kwamitin bincike ya mika sakamakon bincikensa ga Shugaban ƙasa, kuma za a gurfanar da waɗanda aka samu da laifi a gaban kotun soja.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!