Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ina goyon bayan bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai – Jonathan

Published

on

Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya bukaci majalisun dokokin tarayya da su gaggauta ayyana dokar da za ta bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai.

 

A cewar tsohon shugaban kasar kamata ya yi dokar ta bai wa kananan hukumomin ‘yancin neman kudaden shiga da kansu.

 

Goodluck Jonathan ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke zantawa da shugabannin kungiyar ma’aikatan kananan  hukumomi ta kasa NULGE wadanda suka kai masa ziyara gidansa da ke garin Otuoke a jihar Bayelsa.

 

Tsohon shugaban kasar ya ce da shi dan majalisa ne da abin da zai yi shine neman goyon bayan abokansa don bai wa kananan hukumomi ‘yancin gashin kai.

 

A cewar Jonathan al’ummar da ke yankunan kananan hukumomi suna da ‘yancin amfana da dukiyarsu, a don haka  ba daidai bane dukiyoyinsu  su rika makalewa a jihohi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!