Connect with us

Labarai

INEC za ta gana da masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar PDP

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, za ta gana da masu ruwa da tsaki na Jam’iyyar adawa ta PDP yau Talata dangane da taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a ranar 30 ga watan nan da muke ciki na Yuni.

 

Hakan na cikin wata sanarwa da hukumar ta INEC ta mika wa shugaban jam’iyyar ta PDP Ambasada Umar Damagum.

 

Wannan dai na zuwa ne biyo bayan takaddamar da ta kunno kai a tsakanin hukumar da kuma jam’iyyar ta rashin bin ka’idojin gudanar da taron na PDP.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!